Da sanyin safiyar ranar Lahadi ne wasu ‘yan bindiga suka yi yunkurin kai hari kan al’ummar Kunga da ke karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato amma jami’an tsaro sun dakile yunkurin, duk da cewa mutane biyu sun jikkata.
Kunga yanki ne dake kusa da Yelwan Zangam, dukkansu sassa ne na al’ummomin da ke karbar bakuncin rukunin dakunan kwannan dalibai (Naraguta Campus) na Jami’ar Jos.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yajin Aiki: FG Ta Maka ASUU A Kotu Yayin Da Tattaunawar Ta Ruguje
Wannan dai ba shi ne karon farko da Kunga yake fuskantar wata barazana ta tsaro ba, a ‘yan shekarun baya wasu ‘yan bindiga sun mamaye al’ummar garin inda suka kori mazauna garin tare da kona wuraren ibada da gidaje da sauran dukiyoyi.
Wasu daga cikin wadanda suka tsira daga harin na gudun hijira, suna zaune tare da ‘yan uwa a wasu al’ummomi yayin da har yanzu ba a sake gina gidajensu ba.
Wani dan unguwar ya bayyana cewa, “An kai hari a unguwar Kunga ‘A’ da ke kusa da Yelwan – Zangam dake kan hanyar Bauchi bayan dakunan kwanan dalibai na Jami’ar Jos Naraguta da misalin karfe 12:00 na safe. Sai da jami’an ‘yan sandan Najeriya suka shiga tsakani (duk da cewa sun dan makara) don kwantar da hankula. An kwantar da mutane biyu a asibiti, ana ci gaba da bincike da ceto ‘yan sanda, kungiyar mafarauta da kuma ‘yan banga.”
Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alfred Alabo, ya tabbatar da faruwar lamarin, “Jami’an mu sun kai daukin gaggawa, kuma suna yin duk mai yiwuwa don ganin an samu zaman lafiya a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP. Bartholomew Onyeka, Rundunar tana son gode muku don yin wannan kiran akan lokaci.”
“Muna kuma son ku sani cewa ta wannan bayanin da aka bamu a wancan lokaci mai tsanani da aka ceci rayuka da dukiyoyi, wannan ya nuna cewa ku mai gadin dan’uwanku ne, muna cewa muna godiya kuma muna rokon ku da ku kara kaimi a wannan yaki da muggan laifuka da kuma aikata laifuka a Filato.”
Ya kuma tabbatar wa mazauna garin cewa “ba ku da wani abin damuwa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Bartholomew Onyeka ya yi isassun tsare-tsare na tsaro don tabbatar da cewa komai ya daidaita kuma kowa yana cikin koshin lafiya a ciki da wajen al’ummar Kunga ‘A’.”
A wani labarin kuma, NDLEA Ta Kama Wani Dan Kasar Brazil Dauke Da Sinki 92 Na Hodar Iblis
Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, sun kama wani dan kasar Brazil da ya dawo gida kuma mahaifin ‘ya’ya biyu, Okolie Paulinus Nwabueze a filin jirgin saman kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe NAIA dake Abuja bisa laifin shigo da hodar iblis casa’in da biyu (92), wanda ya hadiye kuma a karshe ya fitar da ita bayan kwanaki ana lura da shi a cibiyar Hukumar.
An kama matashin mai shekaru 53 da haihuwa wanda ya fito daga kauyen Mmaku, karamar hukumar Awgu ta jihar Enugu a ranar Juma’a 2 ga watan Satumba a lokacin da ya isa jirgin Qatar Airline da ke kan hanyar Brazil-Doha-Abuja.