Bataliyar Rundunar Sojin Nijeriya ta, Operation Lafiya Dole (OPLD), ta kaddamar da wani shiri na tantancewa domin kama ‘yan ta’addan Boko Haram da na ISWAP da suke tserewa daga shiyyar ta arewa maso gabas.
Mataimakin daraktan hulda da fararen hula na rundunar, Kanar Ado Isa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.
Ya bukaci al’umma da su rika daukan takardun shaidansu a kowane lokaci idan za su yi tafiya zuwa ko fita daga Jihohin Adamawa, Borno da Yobe.
Isa ya ce ana aiwatar da shirin tantancewar ne domin yin bincike da kama ‘yan ta’addan da a yanzun haka suke bin wasu sassan na arewa maso gabas.
Hakan a cewar sa, ya zama tilas a sakamakon ingantaccen rahoton da rundunar ta samu cewa, ‘yan ta’addan da suke tserewa suna rakube ne a wasu garuruwa da kauyaku na Jihohin Borno da Yobe musamman da ma sashen na arewa maso gabas.
Kakakin rundunar Sojin ya bayyana cewa an umurci dakarun Sojin da su tsananta bincike a kan asalin tantance mutane kafin su bar su su ci gaba da tafiye-tafiyen su.
Ya shawarci al’umma da a kowane lokaci su rika daukan takardun tantancewar su, katunan kada kuri’unsu, lasisin tukin su da kuma fasfunansu na fita kasashen kaje domin tantance su a kan lokaci.