Shugaban kasa Muhammad Buhari yayi Allah wadai da daukar doka a hannu wajen kisa wata daliba, Deborah Samuel, dake karatu a kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari dake Jihar Sokoto.
Wasu matasa ne dai suka kashe dalibar bayan sun zarge ta da yin batanci ga shugaban halitta (SAW), inda suka jefe ta da dutsuna har ta mutu, kuma daga bisani suka kone gawarta.
Mai magana da yawun shugaban kasar Garba Shehu, a wata Sanarwa da ya fitar ya ce shugaba Buhari ya kuma bukaci a gaggauta kamo wadanda suka aikata wannan hukunci na hallaka dalibar.
Sanarwar ta kara da cewa wajibi mutum ya girmama Annabi S.A.W, da kuma Annabi Isa A.S, amma kuma bai kamata dan ana zargin wata da batanci gare su a dauki doka a hannu wajen kisan ta ba.
A cewar sa, samun labarin dokar da daliban suka dauka da hannunsu abun tashin hankali ne, yana mai cewa tuni ya bayar da umarnin ganin an kamo su tare da aiwatar da abinda ya kamata akansu.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa tun bayan faruwar Lamarin a jihar, Gwamnatin Jihar ta bayar da umarnin rufe makarantar, tare da gudanar da bincike kan wannan batu.