An tsige ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang daga mukaminsa a ranar Talata bayan da ya bace daga idon jama’a tsawon wata guda, ba tare da wani cikakken bayani daga jam’iyyar gurguzu mai mulki ba, kamar yadda Kafofin yada labaran kasar suka rawaito.
Rashin zuwan Qin wajen aiki ya haifar da cece-ku-ce kan cewa dan shekaru 57, wanda ake daukarsa a matsayin amintaccen shugaba Xi Jinping, ya fadi ne daga bakin aiki ko kuma an gudanar da bincike a hukumance.
KARANTA WANNAN: Kotun Ta Tabbatar Da Hanga A Matsayin Zababben Sanatan Kano Ta Tsakiya
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin a baya ta ce “dalilan kiwon lafiya” ne ke da laifin amma kwanan nan ta ki bayar da wani karin bayani duk da maimaita tambayoyin.
Kafar yada labarai ta kasar Sin Xinhua ta fada a yammacin jiya Talata cewa, babbar majalisar dokokin kasar Sin ta kada kuri’ar tsige Qin daga mukaminsa tare da maye gurbinsa da maigidansa Wang Yi.
Har yanzu dai ba’a bayar da dalilin tsige Qin daga mukaminsa ba amma ya ce Xi ya sanya hannu kan umarnin shugaban kasa na zartar da shawarar.
Da aka tambaye ta akai-akai game da Qin da farko a ranar Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Mao Ning ta shaida wa manema labarai cewa ba ta da “bayanan” da za ta bayar kuma ta nace cewa “ayyukan diflomasiyya na kasar Sin na ci gaba”.
A wani labarin kuma, Fusatattun Matasa Sun Kona Fastar Davido Saboda Wani Faifan Bidiyo
Wasu matasa sun soma kona wata fastar da ke dauke da hoton mawakan afrobeats, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, a wani mataki na nuna bacin ransu kan wani faifan bidiyo da ya wallafa daga bisani kuma ya goge.
Faifan bidiyan mai taken ‘Jaiye Lo’ wanda takwaransa, Olalekan Taiwo, aka Logos Olori ya fitar ya haifar da cece ku ce a Kasar nan.