Rahotanni sun tabbatar da cewa jami’an rundunar soji atisayen ‘Thunder Strike’ sun kubutar da daliban makarantar Sakandire ta jeka ka dawo da ke garin Gwagwada a karamar hukumar Chikun, jihar Kaduna, da aka sace a kan hanyarsu ta zuwa makaranta da safiyar ranar Alhamis.
Mataimakin Daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya da ke Kaduna, Kanal Ezindu Idimah, ya tabbatar da kubutar da daliban ga manema labarai a Kaduna a jiya Alhamis.
Idimah ya bayyana cewa dakarun soji sun kubutar da wasu yaran mota su uku tare da kashe hudu daga cikin masu garkuwa da mutanen.