Daga: Muhammad Gambo Damaturu
- Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya sanya ranar gudanar da zaben kananan hukumomin jihar.
- Hakan ya biyo bayan toron masu ruwa da tsaki inda aka gabatar da bayanai da dama kan yadda zaben zai gudana.
- Dukkan dan jihar Yobe ya cancanta ya yi takarar neman kujera daga matakin Kansila har zuwa Ciyaman matukar ya cika sharuddan zama dan takara.
Biyo bayan bada umarni da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni yayi, cewa a gudanar da zaben kananan hukumomi 17 na jihar a watan Nuwamban wannan shekara, tuni hukumar zabe mai zaman kanta a jihar ta soma shiri.
Shugaban Hukumar Dr. Mamman Muhammad a ranar 2 ga watan Yuni ya kira taron manema labarai da sauran masu ruwa da tsaki inda ya gabatar da bayanai da dama kan yadda zaben zai gudana.
KARANTA WANNAN: Tallafin Fetur: Za Mu Sake Duba Mafi Ƙarancin Albashi Don Yin Tunani Na Gaskiya — Tinubu
Yace, hakan na kunshe ne a cikin kundin dokokin Najeriya na shekarar 1999 a sashe na 197, yana mai cewa Kafafen sadarwa zasu yada labarai kan yadda za’ayi zabukan.
“Jami’an Tsaro kuwa zasu tabbatar da cewa an bada cikakken Tsaro a rumfunan zabe, inda sauran masu ruwa da tsaki zasu taka tasu rawar wajen ganin cewa aikin ya gudana lafiya.
Dr. Mamman ya kara da cewa akwai bukatar a samu cikakken hadin kai da goyon baya domin samun nasarar yin zaben a ranar 25 ga watan Nuwambar 2023.
Yace “Dukkan dan jihar Yobe ya cancanta ya yi takarar neman kujera daga matakin Kansila har zuwa Ciyaman matukar ya cika sharuddan zama dan takarar wanda suke a jere kamar haka:
“Ya kasance ya cika shekara 25 zuwa 30 da haihuwa mace ko namiji, -Ya zama mai hankali – Bashida laifin almundahana.
-Mazaunin yankin da yake neman shugabanta ne, -Yana da karancin matakin karatu a kalla gaba da firamare.
Bayan wadannan sharuddan sun cika, za a sayi takardar neman takara akan naira dubu 300, 250 da kuma dubu 200 a matsayin Chiyaman, Mataimakin Chiyaman da Kansila kamar yadda suke a jere.
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa zaben zai lashe tsabar kudi har Naira Miliyan 700.
A wani labarin kuma, Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Shiga Ganawa da Gwamnonin G5 a Fadar Gwamnati
Tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, tsohon gwamnan jihar Delta tsakanin shekarun 1999-2007, James Ibori, da gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo sunyi dirar mikiya Abuja.
’Yan babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Makinde da Wike ana daukar su a matsayin abokan shugaba Tinubu.
Kazalika sun taka rawa wajen tabbatar da nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu.