Wasu ‘yan bangar siyasa da ‘yan daba a ranar Litinin sun kai hari kan ayarin yakin neman zaben gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola.
‘Yan barandan sun kuma kai hari kan motar bas din wakilin kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) da ke cikin ayarin gwamnan.
Harin da yafi wata motar bas din wakilan kungiyar NUJ ta Osun a unguwar Arapajo da ke Gbongan.
Shedun gani da ido sun bayyana cewa suna dauke da gatari, duwatsu da kuma sanduna.
A rikicin da ya biyo baya, an lalata wasu motoci kusan goma.
Lokacin da motar bas din na NUJ wasu mutanen da ke cikin motar sun samu raunuka daban-daban.
Comments 1