Daga Mu’azzam Yakubu Sanka
Anyi sasanci tsakanin fitattun jaruman Kannywood dinnan guda biyu, wato Ali Nuhu da Adam A. Zango a jihar Kano. Hadaddiyar kungiyar masu shirya finafinan Hausa ta kasa, wato MOPPAN, karkashin jagorancin Malam Abdullahi Maikano ce ta yi wannan aiki a ofishin dattijon Kannywood kuma shugaban majalisar amintattu na kungiyar, wato Malam Abdulkarim Mohammed a yau Asabar. Sakataren kungiyar MOPPAN reshen jihar Kano, Malam Salisu Officer, shi ne ya tabbatarwa da Wakilin mu wannan lamari, ya kuma kara da cewa, yanzu Ali zai janye karar da ya shigar kotu kan Adamu.
A dakace mu don jin karin bayani.…