Fadar shugaban kasa ta ce da wuya majalisar dokokin kasar ta yi watsi da matakin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka kan kudirin gyaran dokar zabe saboda biyayyar jam’iyya.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina, a wata hira da yayi a cikin shirin siyasa a gidan Talabijin na Channels TV mai suna “Sunday Politics”, ya bayyana cewa yin hakan zai zama rashin hakki na ‘yan majalisar a jam’iyyar (APC) yin hakan ya sabawa ra’ayin Mista Buhari a kan haka daftarin doka mai cike da takaddama.
APC, jam’iyyar shugaban kasa ce ke rike da rinjaye a majalisar dattawa da ta wakilai.
Mista Buhari, a makon da ya gabata, ya ki amincewa da kudurin dokar zabe, kwanaki 30 bayan da majalisar ta mika masa a ranar 19 ga watan Nuwamba.
Saboda maganar zaben fidda gwanin kai tsaye da ke cikinta, Mista Buhari, wanda ake ganin gwamnonin jihohi ne suka yi masa tasiri, ya ki amincewa da kudirin.
Ya bayyana rashin tsaro, tsadar gudanar da zaben fidda gwani kai tsaye da kuma take hakkin ‘yan Najeriya na shiga harkokin mulki a matsayin dalilansa na kin amincewa da kudirin.
Wasu daga cikin ‘yan majalisar da ke jam’iyya, kafin su tafi hutu, sun yi barazanar yin watsi da matakin shugaban kasar bayan ya dawo aiki a watan Janairun 2022.
Sai dai Mista Adesina ya yi watsi da yiwuwar ‘yan majalisar na aiwatar da barazanarsu, ganin yadda jam’iyyar APC ke da rinjaye a majalisun biyu.
Ya yi watsi da yiwuwar sake bullowar al’amura inda ‘yan majalisar a jam’iyyar suka yi wa shugaban kasa kaca-kaca a kan wasu muhimman batutuwa a lokacin da Bukola Saraki ya jagoranta.
“Kada mu manta cewa majalisar nan ta kasa musamman ta kunshi fiye da 70, kusan kashi 80 cikin 100 na ‘ya’yan jam’iyyar APC kuma ba ku da wata jam’iyya da za ta durkusar da kanta.
“Ba kamar Majalisar Dokoki ta baya ba da kuka samu ‘yan adawa a jam’iyyar. A’a, wannan shi ne mafi girman alhaki da kuma alhakin Majalisar kasa kuma za su yi abun da ya dace da dimokuradiyyar mu. Za su yi abun da ya dace ga jam’iyyar. Za su yi abun da ya dace ga kasa.
“To, kawar da kujerar na kin wani bangare ne na dimokuradiyya ko kuwa abu ne da ya dace a yi a wani lokaci? Tambayar kenan. Abun da jam’iyyar APC za ta yi amfani da rinjayen da take da shi a Majalisar Dokoki ta kasa kenan. Shin yana da kyau a soke shugaban kasa? Idan ba haka ba, to menene sauran zaɓuɓɓuka? Abun da ya kamata a duba kenan?” yayi gardama.