Wata kotu a birnin Beirut na kasar Lebanon ta bayar da umurnin da a garkame Daraktan Kwastan na Lebanon da kuma Daraktan Tashar ruwan bayan fashewar wadansu abubuwa da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama, da jikkatar dubban mutane.
Kamfanin dillancin labaran Lebanon ne ya labarto hakan. Bayanai sun nuna cewa; akalla mutum 154, a yayin da mutum sama da 4, 000 suka jikkata, a yayin da dama suka bace kamar yadda ma’aikatar lafiyar kasar ta tabbatar.
Rahotanni sun nuna cewa za a garkame Daraktan Kwastan din na Lebanon, Badri Daher da kuma tsohon Daraktan Kwastan din, Shafik Merhi, da kuma Daraktan tashar ruwan Hassan Kuraitim har sai an kammala bincike kan lamarin.
A ranar Alhamis ne, aka garkame mutum 16 kan fashewar abubuwan a tashar ruwan ta Beirut.
Bayanai sun nuna yadda masu aikin ceto ke ta fafutikar cire baraguzai domin ‘yanto wadanda aka rubde a kasa.
Ma’aikatan lafiya ta Red Cross ta Lebanon, ta bayyana cewa sun yi imanin cewa mutum 100 sun bace har yanzu ba a gano su ba. Wadanda mafi yawansu suna aiki a tashar ruwan ne.
Gidaje da dama da ababen hawa fashewar abubuwan ya tarwatsa su. Inda bayanai suka nuna cewa fiye da gidaje 250, 000 lamarin ya shafa.
Shugaban Lebanon Michel Aoun ya yi alkawarin binciko abin da ya faru, inda ya ce za a binciki hatta manyan jami’an gwamnatin kasar.