A yammacin yau ne Gwamna Nasir Ahmad El’rufa’i tare da Sanata Malam Uba Sani da rakiyar tawagarsa Suka Kai ziyara Zuwa ga helkwatar Jam’iyar APC dake Abuja kamar yadda Sanata Uba Sani ya Bayyana dalilin ziyarar tasu Yana Cewa A yau, na raka gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i mai kaifin basira da hazaka zuwa hedikwatar jam’iyyar APC dake Babban birnin tarayya Abuja Domin ganawa da manyan Shugabannin jam’iyyar kan batutuwan da suka shafi cigaba da nuna kwarin gwiwa da wadatar da tsarin jam’iyyar a jihar Kaduna.
Tawagar ta samu kyakkyawar tarba daga Sakataren Kwamitin Tsare -Tsare na Musamman na Jam’iyar ta APC, Sanata Akpan Udoedehe. A yayin da yake jawabi Gwamna El-Rufai ya nuna farin cikinsa da tarba da aka yiwa tawagar tasa kuma ya nanata biyayarsa akan nuna fifikon jam’iyyar da mahimmancinta wajen gina al’umma da samar da ci gaba da kuma ƙarfafa tsarin demokraɗiyya Ya bayyana cewa jam’iyyar tana da hanyoyin acikinta da ka iya kawar da damuwa da korafe -korafen membobin jam’iyyar da kuma warware wasu batutuwan.
Gwamnan Wanda ya Kasance mai son dorewar cigaban al’umma ya shaida wa jami’an APC cewa a matsayinsa na jagoran APC a jihar Kaduna zai ci gaba da tabbatar da hadin kai da adalci a tafiyar ta jam’iyyar APC Haka kuma Za a ci gaba da ɗaukar membobin jam’iyyar a cikin tsarin shawara tare da Jagoranci na gama gari shine mabuɗin ci gaban jam’iyya domin dunkulewa waje ‘daya.
A nasa bangaren sakataren tsare Tsare na Jam’iyar Sanata Akpan Udoedehe ya tabbatar wa Gwamna El-Rufai da tawagarsa goyon bayan Kwamitin rikon kwaryar na APC a kokarinsa na mayar da Jam’iyyar APC ta Jihar Kaduna a matsayin na’urar tantance sahihin zabe. Ya kuma ce Kwamitin zai yi nazari mai zurfi kan batutuwan da wakilan suka gabatar tare da magance su cikin gaggawa. Inji Sanata Uba Sani.
Jam’iyar APC a jihar kaduna itace ke mulkin jihar kaduna Malam Nasir Ahmad El’rufa’i shine Gwamna wanda ya Kasance amini ga Sanata Malam Uba Sani Mai wakiltar kaduna ta tsakiya a majalisar dattijan Nageriya ziyarar tasu na zuwa helkwatar Jam’iyar na da nasa ba ga Neman hanyoyin zaman lafiyar Jam’iyar da ‘yan Jam’iyar a jihar kaduna..