Wakilinmu Mohammed Gambo Damaturu
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bada tabbacin aiwatar da duk abun da Kwamitin duba lamuran fensho a jihar ta zayyana a rahoton ta.
Ya bada tabbacin hakan ne yayin da yake amsar rahoton Kwamitin wanda shugaban Kwamitin Alhaji Rabiu Zakariya ya mika masa.
Wata sanarwa da ta fito daga ofishin mai magana da yawun mataimakin Gwamna Hassan Musa Face, wacce aka bayyanawa Jaridar Dimokuradyya ta yi nuni da cewa hakan zai tsarkaka yanayin biyan Pensho.
A rahoton Kwamitin an gano matasalloli da dama cikin harkar don haka ne ma, ya sa aka dorawa Kwamitin alhakin duba lamarin.
Ganduje ya yaba da irin kokarin da sukayi wajen tattara dukkan bayanai tare da nemo musu maslaha.
Idan za’a iya tunawa Ganduje ya kaddamar da Kwamitin ranar 23 ga watan Nuwamba na shekarar 2018 ta inda ya daura mata nauyin kawo hanyoyin gyara ga yanayin biyan fensho.