Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi ya biya Naira miliyan 100 da ake bukata domin siyan fom din tsayawa takara na jam’iyyar APC don tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Yemi Kolapo, mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa Yahaya Bello ce ta bayyana hakan a ranar Talata a wata sanarwa da ta rabawa manema labarai.
Misis Kolapo ta ce gwamnan ya biya kudin ne a safiyar ranar Talata a wani yunkuri na nuna muhimmancinsa ga ‘yan Najeriya a yunkurinsa na fitowa takara a jam’iyya mai mulki.
Ta bayyana cewa gwamna Bello zai kasance a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja domin karbar fom din a ranar Laraba.
Darakta Janar ta kungiyar yakin neman zaben, Hafsat Abiola-Costello, ta tabbatar wa jaridar PREMIUM TIMES hakan a ranar Talata.
Gwamna Bello dai ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a ranar 2 ga watan Afrilu a dandalin Eagle Square da ke Abuja.
Yayin da yake bayyana sha’awarsa ta tsayawa takara, Gwamna Bello ya yi alkawarin samar da attajirai miliyan 20 ƴan Nigeria, idan aka zabe shi.
Idan dai ba a manta ba, kwamitin ayyuka na jam’iyyar na kasa ya fitar da sabuwar ranar sayar da fom, bayan da ta kasa cika wa’adin farko da majalisar zartarwa ta kasa ta kayyade.
An canza kwanan wata daga Afrilu 23 zuwa Afrilu 26.
Hukumar zaben ta kuma ware Naira miliyan 100 a matsayin kudin takarar shugaban kasa da bayyana fom din takarar ta, duk da cewa wannan mataki na jam’iyyar ya sha suka.