- Gwamnatin jihar Kano ta amince da naira miliyan 854 domin gudanar da aurar da mata masu karamin karfi
- Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka bayan taron majalisar zartarwa ta jihar Kano a ranar Laraba 23 ga watan Agusta
- Yusuf ya ce an amince da Naira miliyan 854 ne na kashi na farko na shirin bikin aure na Auren Zaurawa.
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, ya bayyana shirin ɗaukar nauyin ɗaurin aure a tsakanin marasa galihu tare da amincewa da Naira miliyan 854.
An yanke shawarar ɗaukar nauyin ɗaurin auren ne yayin zaman majalisar zartarwa ta jihar a ranar Laraba, 23 ga watan Agusta.
Gwamna Yusuf ya bayyana haka ta hanyar sahihin asusun sa na Twitter @Kyusufabba a ranar Alhamis, 24 ga watan Agusta.
KARANTA WANNAN LABARIN: Jami’ar Chicago Ta Amince Da Fitar Da Bayanan Karatun Tinubu Bayan Bukatar Atiku, Ta Bayar Da Sharaɗi – Dimokuradiyya
Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da hakan: “Sakin Naira miliyan 854 na kashi na farko na bikin aure na Auren Zaurawa.” Auren taro na ma’aurata 1,020
A cewar majiyarmu, kwamandan Hukumar Hisbah na Jihar, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, a baya ya ce ana ci gaba da shirye-shiryen gudanar da daurin aure ga ma’aurata 1,020 masu sha’awar shiga a fadin jihar.
Daurawa ya ce taron daurin auren na jama’a za a yi shi ne domin a taimaka wa ma’auratan da ba za su iya biyan kudin aure ba saboda wahalar rayuwa.
Ya bayyana cewa za a zabo ma’aurata 20 daga kowace karamar hukuma 44 sannan hukumar za ta zabi sauran ma’aurata 120.
Gwamnatin Kano Za Ta Biya N700m Ga Daliban BUK, N854 Don Auren Zawarawa
A wani labarin kuma: Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da fitar da Naira miliyan 700 don biyan kudin makarantar ‘yan asalin Kano 7,000 da ke karatu a Jami’ar Bayero Kano.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta tattaro cewa Bugu da kari, an ware Naira miliyan 854 don shirin bikin Auren Zaurawa a jihar.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a shafinsa na X da aka tabbatar, wanda aka fi sani da Twitter.
Gwamnan ya ce amincewa da Naira miliyan 700 ga daliban Kano a makarantar BUK an yi shi ne a yayin taron majalisar zartarwa ta Jiha a ranar Larabar da ta gabata kan matsalar tattalin arzikin da kasar nan ke fama da shi.
“A wani bangare na kokarin da muke yi na ganin an dakile illar tattalin arzikin da muke ciki a halin yanzu.
“Majalisar zartaswar jihar Kano karkashin jagorancina ta amince da fitar da Naira miliyan 700 domin biyan kudin karatar dalibai 7,000 na Jami’ar Bayero Kano.” inji gwamna.