Gwamnan Neja ya baiwa ‘yan banga makamai da bindigogi don yakar’ yan fashi

Gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya yi alkawarin samar da bindigogi ga kungiyoyin ‘yan banga domin taimakawa wajen takaita matsalolin rashin tsaro a jihar.
A yayin ziyarar bazata, Gwamnan ya shirya ganawa da mambobin kungiyar banga sama da 200 a kauyen Kasuwan Garba da ke jihar, inda ya tabbatar masu da cewa zai taimaka musu da bindigogi don yakar ‘yan bindigar da ke addabar jihar.
Yin fashi da makami, da satar mutane suna Nema su zama ayyukan yau da kullun a cikin jihar Neja, kamar yadda ake ganin hare-haren baya-bayan nan na sace dalibai da ma’aikatan Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Kagara da wasu matafiya.
Duk da dai An saki dukkan wadanda lamarin ya rutsa da su bayan tattaunawar da aka yi da ‘yan bindigar.
Amma wasu ‘yan bindiga a Nijar da jihohi makwabta sun la’anci kungiyar’ yan bangan kuma sun Ce zasu ajiye makamansu idan gwamnati da gaske take yi game da yarjejeniyar zaman lafiyar.