Gwamnatin Filato ta nuna farin cikinta game da inganta allurar rigakafin cutar Korona a fadin jihar, Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa, Mista Dan Manjang, ya bayyana hakan.
Manjang ya bayyana hakan ne a yayin wani taron manema labarai a karshen taron majalisar zartarwa ta jihar a gidan gwamnati dake Jos a ranar Laraba.
Ya ce bayanai sun nuna cewa karin mazauna yankin suna yin aikin rigakafin cutar, yana mai cewa, “fitowar mazauna don yin allurar rigakafin da gwajin COVID-19 yana karfafawa duk da kaidin makirci”.