Gwamnatin Jihar Neja ta biya Naira miliyan 205 da Hukumar shirya jarabawar kammala sakandare ta Afirka ta Yamma (WAEC)take binta,ta biya a kudaden jarrabawar kammala sakandare (SSCE).
Mataimakiya ta musamman ga gwamna Muhammad Umar Bago kan harkokin yada labarai, Ms Aisha Wakaso, ta bayyana hakan a wani taron manema labarai a Minna, babban birnin jihar.
A cewarta, gwamnatin jihar ta yanke shawarar biyan bashin ne domin ganin an fitar da sakamakon jarabawar WAEC na daliban jahar da hukumar ta hana.
Karanta nanZamu Gaggauta Amincewa Da Kasafin Kudin Bana Idan Yazo Hannunmu-Majalisar Wakilai
Ya zuwa yanzu sakamakon daliban jihar Neja ba su fito ba saboda basussukan da ake bin jihar na tsawon lokaci inji ta.
Mai taimaka wa Gwamnan ta kuma bayyana cewa gwamnati ta karbi samfuran motocin dakon iskar gas (CNG) da za a sayo domin rage matsalolin sufuri da jama’ar jihar ke fuskanta.
Ta kara da cewa nan ba da dadewa ba za a kai motocin guda 200 da jihar ta bayar ga wadanda suka kamata domin fara jigila dasu.
A wani labarin kumaMijina Yana Iyakar Kokarinsa Wajen Ganin An Sako Daliban Gusau-Matar Gwamnan Zamfara
Idan dai za a iya tunawa gwamnatin jihar ta kulla yarjejeniya da wasu kamfanoni hudu na kwangilar sayen motocin bas na CNG akalla 200 a kan Naira biliyan 7 don rage wahalhalun da ke tattare da cire tallafin man fetur don samar da sufuri kyauta ga dalibai da dalibai a jihar.
Gwamna Bago, yayin rattaba hannu kan yarjejeniyar a watan Satumba na 2023, ya ce ana sa ran kammala jigilar motocin bas din nan da makonni 12.