Wakilinmu Ahamed Musa Gumel
Gwamnan jiha Jigawa Muhammad Badaru Abubakar rantsar da Khadi Isah Jibrin Gantsa a matsayin alkalin’alkalan kotun daukaka kara ta shari’ar Musulunci.
A jawabinsa wajen bikin da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar jigawa dake Dutse, Gwamnan ya yabawa Majalisar kula da al’amuran shari’a ta kasa da babban mai shari’a na jihar jigawa bisa tabbatar da nadin, Khadi Isah Jibrin Gantsa a matsayin grand khadi.
Alhaji Badaru Abubakar ya bayyana Khadi Isah Jibrin Gantsa a matsayin daya daga cikin hazikan alkalin alkalai a tarihin jihar Jigawa.
Daga nan Gwamnan ya shawarci sabon alkalin-alkalan ya kasance mai gaskiya da adalci wajen gudanar da aikinsa,tare da yi masa fatan alheri a tsawon wa’adin aikinsa.
Babbar Sakatariyar ma’aikatar shari’a, mai shari’a Hauwa Zakar ta kaddamar da rantsar da sabon alkalin alkalan kamar yadda yake kunshe a kundin tsarin mulkin Kasa na shekara ta 1999.
A ranar talatar da ta gabata ne majalissar dokokin jihar jigawa ta tabbatar da nadin sa
Bikin rantsar da alkalin alkalan ya samu halartar mataimakin gwamnan jiha Alhaji Umar Namadi da babban mai shari’a na jiha Aminu Sabo Ringim da shugaban Majalisar dokokin jiha Alhaji Idris Garba da Mai martaba Sarkin Dutse Dakta Nuhu Muhammad Sunusi da Alkalai da kuma iyalai da yan uwa da abokan arziki.