By Abbas Yakubu Yaura
Kwamishinan Kudi na Jihar Jigawa, Ibrahim Umar, ya ce jihar ta samu tallafin naira biliyan 13.5bn daga rancen dalar Amurka miliyan 750 da Bankin Duniya ya baiwa gwamnatin tarayya ga gwamnatocin jihohi ta hanyar tsare-tsare na kasafin kudi na jihohi.
Umar ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan aiwatar da shirin gwamnatin tarayya na SFTAS da bankin duniya ke taimakawa.
A cewar kwamishinan, jihar Jigawa ta taka rawar gani a shirin na SFTAS kuma ta ci gajiyar tallafin naira biliyan 13.5bn a tantancewar shekarar 2018 zuwa 2019.
Sannan ya kara da cewa za a yi tantancewar na shekarar 2020 ne a ranar 26 ga watan Fabrairun wannan shekara, yayin da na shekarar 2021 za a yi a watan Yuni.
Gwamnan jihar Jigawa, Mohammed Badaru, ya danganta karancin basussukan da jihar ke fama da shi a kan tsarin kasafin kudi, yin gaskiya da rikon amana wajen amfani da albarkatun kasa.
Gwamnan ya ce gwamnatin sa ta yanke shawarar ba za ta ci bashi ba amma ta yi rufa-rufa da kuma bunkasa kudaden shiga da ake samu a cikin gida.“Muna da mafi ƙarancin bayanan bashi a duk ƙasar, Ba mu aro ba. Muna kokarin kiyaye dorewar kasar,” inji shi.
Badaru ya ce shirin na SFTAS ya kara taimakawa jihar wajen ganin an kafa tsarin mulki na gaskiya cikin gaskiya da rikon amana da kuma dorewa.
Ko-odinetan shirye-shirye na kasa, SFTAS, a ma’aikatar kudi ta tarayya da tsare-tsare, Mista Stephen Okon, ya bayyana jihar Jigawa a matsayin daya daga cikin jahohi uku da ke kan gaba wajen aiwatar da shirin na SFTAS.
Okon, wanda ya samu wakilcin mataimakin ko-odineta na kasa, SFTAS, Mista Ali Mohammed, ya ce kafin kaddamar da shirin, gwamnatin Badaru ta bullo da tsare-tsare da dama wadanda suka tanadi tsarin kasafin kudi.