Kwamitin da gwamnatin jihar Kano ta kafa domin zagayen rangadi a gonakin noman rani dake yankunan kananan hukumomin kura garin-malam ya ziyarci yankunan are da tattara sakamakon da ake da bukata domin yanke hukunci, kan kudurin hukumar raya kogunan hadeja jama’are na rufe ruwa a ranar 1 ga watan nuwamba zuwa 30 ga watan maris na wannan shekara.
An dai samar da kwamitin ne bayan da wasu daga cikin manoman yankunan suka shigarwa da gwamnatin jihar Kano, korafi kan irin illar da hakan ka iya haifarwa ga amfanin su na wannan damunar. Duk kuwa da cewa hukumar bata tashi wannan aiki ba sai da ta samu sahalewa daga hukumar bunkasa noman rani, kungiyar manoman, hadi da injiniyoyin da zasu gudanar da aikin a dam din Tiga.
Yanzu haka dai bayan ziyarar gani da ido da kwamitin ya kai, zai zauna domin rubuta rahoto kan abunda suka gani tare da mikawa gwamnatin jiha domin zartar da hukunci na karshe.
Kwamitin dai ya kunshi Daraktan kula da harkokin noma na jihar kano, daraktan kula da madatsun ruwa a ma’aikatar ruwa ta Kano, da Ijiniyan dake sanya ido kan aikin daga hukumar Tremin, mataimakin daraktan mulki da kuma ami’in hulda jama’a a hukumar raya kogunan hadeja jama’are karkashin jagorancin Injiniya Umar Ibrahim Langel wanda shine shugaban kwamitin.