BBC Hausa ta labarto cewa; gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ta ɗauki matakai domin karɓar riga-kafin annobar korona na mutum miliyan 20 zuwa farkon shekara mai zuwa.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ministan lafiya na ƙasar, Osagie Ehanire ya bayar da umarnin buɗe duka wuraren killace waɗanda suka kamu da cutar a faɗin ƙasar, sakamakon ƙaruwar da ake samu na masu kamuwa.