Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), Abdullahi Malam Muhammad, ya kaddamar da kwamitin tsaro wanda zai duba aikin Hajin shekara ta 2019. Mai magana da yawun Hukumar ta NAHCON, Fatima Sanda Usara, ce ta bayyana haka a jiya juma’a a cikin wani jawabi da ta yi, in da ta ce, Hukumar ta kafa kwamitin na mutum goma wanda zai kula da tsaron aikin Haji na bana. Haka kuma ta ci gaba da cewa, kwamitin ya kunshi jami’an tsaro da hukumomin tsaro da ke kasar nan. Sauran sun hada da ma’aikata na musamman daga ofishin sakataren gwamnatin tarayy da jami’an kwastam da jami’an kula da shigi da fice da jami’an Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi, da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara da Hukumar kiyaye hadurra ta kasa, dukkanin wadannan Hukumomin an dora musu nauyin kula da harkar tsaron aikin Hajin bana tun daga farkonsa har zuwa kamala shi. “Haka kuma aikin nasu ya hada da tattara bayanai wadanda za su mikawa Hukumar domin yin amfani da su nan gaba. Shugaban Hukmar ya ci gaba da cewa, babbar manufar kafa wannan kwamiti shi ne ya tabbatar da martabar kasar nan a idon duniya ta hanyar tabbatar da cewa, dukkan mahajjata sun kiyaye dukkannin dokokin da suka kamata su bi a cikin kasa da kuma lokacin da suke Kasa maitsarki,”.