Firaministan Lebanon, Hassan Diab ya yi murabus biyo bayan tayar da jijiyar wuya a ciki da wajen gwamnatinsa, sakamakon mummunar fashe fashen sinadarai a tashar jiragen ruwan Beirut.
Firaminista Hassan Diab, a wani jawabi da ya yi ga al’ummar kasar ya ce ya zama wajibi ya yi aiki da muradan al’ummar kasar, saboda haka yake sanar da cewa gwamnatinsa ta yi murabus.
A game da fashe fashen da suka auku a ranar 4 ga watan Agusta kuwa, Diab, ya zargi rukunin ‘yan siyasa da suka mulki kasar tsawon shekaru 30 da zama ummu’abaisan faruwar lamarin.