Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) reshen jihar Kano, ta ceto tare da mika mutane 27 da za a yi safarar su ga rundunar hadin gwiwa ta rundunar tsaro ta jihar Kano.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Abdullahi Babale, Kwamandan Hukumar yaki da fataucin bil Adama ta kasa (NAPTIP) shiyyar Kano, ya bayyana haka a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Kasa (NAN) a ranar Alhamis din nan a Kano.
KARANTA KUMA: Yan Sanda Sun Kubutar Da Wata MataDa Za A Yi Safararta
Ya ce an dauki wadanda lamarin ya ritsa da su ne daga jihohin Oyo, Osun, Kogi, Ondo, Ekiti, Legas da Ogun.
A cewarsa, wadanda ake zargi da laifin safarar mutane da kuma wanda ake zargi za a yi safarar su an shirya su ne zuwa Libya domin samun aikin yi.
“Sun kasance tsakanin shekaru 19 zuwa 40, tare da mata 23 da maza hudu,” in ji Babale.
Jaridar Solacebace ta rawaito, Ya bayyana cewa hukumar za ta gurfanar da wanda ake zargin tare da hada kan wadanda abin ya shafa da iyalansu.(NAN)
A wani labarin kuma: Sama Da Mitane 360,000 Ambaliyar Ruwa Ta Raba Da Muhallansu
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Nasarawa NASEMA, ta ce akalla mutane 361,000 ne suka rasa matsugunansu sakamakon ambaliyar ruwa sanadiyyar mamakon ruwan sama da aka yi a jihar.
Mista Zachary Allumaga, Sakataren zartarwa na hukumar NASEMA, ya shaida wa manema labarai ranar Alhamis din nan a garin Lafiya cewa ambaliyar ta shafi al’ummomi 23 a kananan hukumomi bakwai na jihar.