Daga Muhammad A. Dalhatu
Hukumar dake lura da jami’o’in Nijeriya, NUC ta nuna gamsuwarta bisa yadda ta ga kayayyakin karatu da gine-gine da aka shimfida a muhallin Jami’ar ‘Maryam Abacha American University of Nigeria, Kano’.
Daraktan hulda da jama’a na hukumar, Malam Ibrahim Usman Yakasai, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a yayin da yake ganawa da manema labarai jim kadan da tawagar hukumar ta ziyarci muhallin Jami’ar domin duba irin tsare-tsare da kayayyakin aiki da ake sanyawa a muhallin Jami’ar ta Nijeriya dake Hotoro cikin kwaryar Kano.
Ya kara da cewa; “kamar yadda kuka sani a yayin da aka nemi assasa sabuwar Jami’a mai zaman kanta kuma aka nemi lasisi a wurinmu, to zamu ziyarci muhallin da aka tanada domin gina jami’ar domin ganewa idonmu gine-gine da kuma kayayyaki da aka tanada domin gudanar da jami’ar. Abin da muka gani a nan, ya gamsar damu”. Ya tabbatar.
Ya ci gaba da cewa NUC za ta ci gaba da karfafawa kan ganin an ci gaba da assasa Jami’o’i masu zaman kansu a kasarnan, domin a cewarsa jami’o’in da ake da su masu zaman kansu da na gwamnati ba su wadatu ba idan aka yi duba da yadda dalibai masu neman gurbin shiga jami’a ke karuwa a duk shekara.
Yakasai har wala yau ya ce samar da masu jami’o’i masu zaman kansu a kasarnan zai bai wa ‘yan kasa damar samun wadatacce kuma ingantaccen ilimi a kasar.
“Akwai dalibai sama da miliyan biyu da suke neman gurbin shiga makarantun gaba da Sakandare a kasarnan a duk shekara a yayin da jami’o’i 177 da ake da su a kasar ba ya iya daukar dalibai su zarce dubu dari biyar (500, 000), a don haka akwai bukatar assasa jami’o’i masu zaman kansu.” Ya lurantar.
Da yake na shi jawabi, tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafizu Abubakar, ya jinjinawa mamallakin jami’ar Farfesa Adamu Abubakar-Gwarzo bisa wannan gagarumin aiki da ya dauko. Inda ya ce al’ummar jihar Kano su godewa Allah bisa ba su Farfesa Gwarzo da ya yi wanda ya zama dan kasa mai kishin jiharsa.
Har wala yau, Farfesa Hafizu, ya shawarci masu hannu da shuni na jihar Kano, da su yi koyi da Farfesa Gwarzo wajen assasa wadansu jami’o’in masu zaman kansu a jihar duba da cewa Kano har yanzu ita ce jihar da ta fi kowanne jiha a kasarnan yawan al’umma.
Ya kara da cewa; “shekaru biyar da suka gabata ban taba tunanin wani a cikin kasarnan zai sanya hannun jarinsa a bangaren ilimi ba kamar yadda wannan jajirtaccen matashin ya yi. Ka duba jihar Ogun duk da kankantar jihar, amma suna da jami’o’i masu zaman kansu guda 18. Dole mu dauki wannan kalubalen domin ganin mun samu ci gaba.” Ya ankarar.
Har wala yau tawagar hukumar NUC din, sun kai ziyara muhallin dindindin na Jami’ar MAAUN ta Nijeriya dake Gwarzo a jihar ta Kano.