By Ishaq Dabai
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), ta yi nasarar kama miyagun kwayoyi iri daban -daban wadanda nauyin su ya haura sama da kilo 153, 256.876 a cikin makon daya gabata.sannan kuma hukumar ta bayyana cewa ta kama mutane 663 da ake zargi a jihohi daban -daban a cikin wannan lokacin.
Hukumar NDLEA ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai, Mista Femi Babafemi, ya fitar ranar Lahadi a Abuja yace daga cikin wadanda ake zargi 663 da aka kama akwai wani dan bautar kasa, dan sanda da wani soja da ake zargi, duk na karya ne.
Yace jami’an hukumar NDLEA sun kai samame gidajen miyagun kwayoyi a Legas, Abuja, Benue da sauran sassan kasar a makon daya gabata, a cewarsa, samamen ya kai ga gano haramtattun magunguna masu nauyin kilo 153, 256.876, wanda ko dai an lalata su ko kuma an kama su.
“An kama mutane 27 da ake zargi, yayin da aka kama miyagun kwayoyi daban -daban kamar hodar iblis, Tramadol, Rohypnol da tabar wiwi, masu nauyin kilogram 2,463.876.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Bababfemi yace an cafke wani da ake zargi Mataimakin Sufeto Janar na ‘yan sanda Joshua Yusuf, wanda ya yi ikirarin yana aiki a Kano, a kan babbar hanyar Gwagwalada yayin da yake dauke da kilo 45.5 na tabar wiwi.Kakakin ya kara da cewa an kama akalla mutane 615 da miyagun kwayoyi, wadanda nauyinsu ya kai kilo 3394.2031, wanda aka gano a simamen da aka kai a sauran garuruwa jihohi.
Bababfemi ya bayyana cewa Shugaban, NDLEA, Mai ritaya Brig.Janar Buba Marwa, kamar yadda ya yabawa hafsoshi da mazajen rundunar jihar Legas da takwarorinsu na Benue, FCT, Ogun, Ekiti da sauran sassan kasar.
Marwa ya yaba musu bisa jajircewarsu wajen yaki da haramtattun abubuwa, inda ya umarce su da kada su huta a kan dokinsu.Ya yi kira da a ci gaba da hada kai tsakanin hukumar da sauran masu ruwa da tsaki, musamman rundunar soji da sauran hukumomin tsaro dan tabbatar da doka.