Hukumar kula da harkokin ruwa a Nijeriya wato NIMASA ta raba kayayyaki ga wadanda guguwa da hare-haren ‘yan ta’adda ya rutsa dasu a cikin wasu kananan hukumomi 5 da ke jihar Zamfara.
Da yake jawabi a lokacin da ake raba kayan a Gusau ranar Asabar, mai bai wa gwamnan jihar shawara akan harkoin agaji, Manjo Aliyu Maradun mai ritaya ya ce akwai kayan abinci da kuma wadanda ban a abinci ba.
Ya ce garuruwan da abin hare-hare da guguwa ya jawo musu asara sun hada da Gusau, Anka, Bukkuyum, Gummi da Maradun
“Sauran kayan da hukumar ta NIMASA ta kawo mana agajinsu sun hada da katifu, taburmai, manja, man gyada da sauran kayan masarufi. Yau za mu raba kayan daga nan Gusau kafin mu je sauran kananan hukumomi hudun da suka rage”, inji shi.
Maradun ya yaba wa hukumar NIMASA a kan wannan kokarin. Sannan ya bukaci sauran mutane da ma’aikatu su yi koyi da ita wajen tallafawa wadanda hadarin ya shafa a jihar.
Ya kuma jaddada manufar gwamnan jihar, Gwamna Bello Matawalle wajen tallafa wa ‘yan gudun hijira da sauran masu bukatar agaji.
Shugaban hukumar mai wucin gadi, Alhaji Bello Mafara ya nemi mutanen jihar da su ci gaba da addu’a ga Ubangiji don sulhun da gwamnatin jiha ta jagoranta ya dore.
Wani dan gudun hijira daga Anguwar Kara da ke karamar hukumar Gusau, wanda ya yi magana a madadin sauran wadanda suka ci moriyar tallafin ya yi godiya ga hukumar NIMASA.