Rundunar ‘yan sandan farin kaya ta Najeriya NSCDC reshen jihar Sokoto ta dakatar da duk wasu ayyuka da suka shafi aikin sa kai a rundunar har sai an kammala binciken da kwamandan Mohammed Sale-Dada ya gabatar.
Hakan ya fito ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSC Hamza Adamu-Illela kuma aka rabawa manema labarai a Sokoto.
Sanarwar ta ruwaito Kwamandan, Mista Sale-Dada yana cewa, dakatarwar ta biyo bayan kama wasu jami’an sa-kai da aka yi a kwanan baya a wani samame na hadin gwiwa da aka yi a dukkan yankunan da ke karamar hukumar Sakkwato ta Kudu.
Kwamandan ya ce halin ‘yan sa-kan da aka kama bai dace ba, kuma bai kamata ba, da nufin bata sunan rundunar, wanda aikinsu shi ne yakar laifuka da hana aikata laifuka a cikin al’umma.
Ya ce ‘yan sa kan da aka kama ba su da rajista da hukumar NSCDC ta jihar Sakkwato, don haka za a yi watsi da su har sai an kammala bincike da bayyana duk ma’aikatan da ke gudanar da ayyukan sa-kai.
Shugaban karamar hukumar Sokoto ta Kudu Faruk Sawidi ne ya jagoranci tawagar jami’an tsaro suka kai wani samamen da suka kai makura a cikin majalisar kuma ana cikin haka an kama wasu jami’an sa kai na hukumar NSCDC a cikin kogon masu aikata laifi a Unguwar Diplomat ta jihar Sakkwato.