Rahotanni da ke shigowa Jaridar Dimokuradiyya sun tabbatar da cewa; Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya ta tallafawa dalibanta 34 da naira miliyan 10 ga wadanda suka samu gurbin karatu kyauta a kasar China domin kammala digirinsu na farko da kuma wadanda za su yi digiri na uku wato PhD a kasar China.
Mataimakin shugaban Jami’ar, Farfesa Ibrahim Garba shi ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi a taron bankwana da aka shiryawa daliban a Samaru dake Zariya a jihar Kaduna.
Rahotanni sun tabbatar da cewa; shirin karatun na karantar bangaren Injiniya ne, kuma tsari tsakanin Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya da kuma jami’ar Central South University (CSU), dake Changsha a China domin su je can su kwashe shekara uku, sannan su dawo Jami’ar Ahmadu Bellon su kara shekara biyu.
Wannan sabon tsarin zai bai wa dalibai damar samun kwalin digiri na farko a a China da Nijeriya a bangaren Traffic Transportation.