By Abbas Yakubu Yaura
Gwamna David Umahi na jihar Ebonyi ya sanar da dakatar da duk wasu ma’aikatan gwamnati daga yankin Effium dake karamar hukumar Ohaukwu da rikici ya daidaita sakamakon kashe wasu ma’aikatan gine-gine guda biyar.
Umahi ya bayyana hakan ne a ranar Talata a Abakaliki yayin gudanar da wani taron tsaro da kungiyar kiristoci ta Najeriya CAN reshen jihar ta shirya kuma iyayen jihar.
Gwamnan ya yi zargin cewa wadanda suka aikata munanan ayyuka a yankin suna samun kudade daga ciki da wajen jihar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “An cire shuwagabannin cibiyoyi biyu na ci gaban kananan hukumomin yankin daga bakin aiki yayin da aka dakatar da albashin sakatarorin dindindin na yankin.
Sannan gwamnan yace “Zan tunkari majalisar dokokin jihar kan hanyar data shafi shugaban karamar hukumar da ‘yan majalisar biyu daga yankin,” in ji shi.
Ya ce masu rike da mukaman siyasa ba za su iya karbar albashi ba don haka za su shiga daukar nauyin kashe-kashe da lalata dukiyoyin mutane.
Umahi ya yi nadamar kisan gillar da aka yi wa wasu ma’aikatan gine-gine guda biyar a titin ring titin jihar wanda wasu da ba a san ko su wanene ba suka bi ta yankin tare da aikata danyen aikin.
“Wadannan ma’aikatan da ba su san komai ba game da rikicin sun je wurin ne domin su taimaka wa jihar wajen gudanar da aikin gina hanyar.
“Wadanda ake zargi da faruwar lamarin sun amsa cewa an kashe ma’aikatan kuma an binne su, sannan an bukaci nemi sanin inda aka binne su domin kwantar da hankalin iyalan wadanda abin ya shafa.
“Rundunar ‘yan sandan da ta ziyarci yankin domin gudanar da bincike an yi musu kwanton bauna kuma an bace ko kuma an kashe wasu ‘yan bindiga guda biyu,” in ji shi.
Umahi ya bukaci masu ruwa da tsaki na yankin da su shawo kan lamarin a cikin kwanaki bakwai domin an kai matakin da ya dace gwamnatin tarayya ta dauki matakin.
Shugaban kungiyar iyayen kasa na jihar kuma tsohon gwamnan jihar, Cif Martin Elechi ya godewa gwamnan bisa amincewa da taron domin an samu sakamako mai kyau daga irin wannan a baya.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa har yanzu ba a gano gawarwakin ‘yan kwangilar ba yayin da ake zargin al’ummar sun kaiwa tawagar ‘yan sanda da suka je tantance su. ya janyo asarar rayuka da dukiyoyi na miliyoyin naira.