….Hukumar zabe ta Kasa INEC ta bada tabbacin sake gudanar zabe cikin nasara a dukkan wiraren da za a sake, yayin da take raba muhimman kayayyakin..
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC), ta ce ta kammala shirye-shiryen gudanar da sake zaben gwamna da na ‘yan majalisar kasa da na jiha cikin nasara a Kebbi.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta ruwaito cewa INEC ta sanya ranar 15 ga watan Afrilu domin sake gudanar da zabukan gwamnoni a jihohin Kebbi da Adamawa da kuma zaben ‘yan majalisar dokoki na kasa da na jihohi a fadin wasu jihohin kasar nan.
Za a sake gudanar da zaben gwamna a rumfunan zabe 142 (PUs) a fadin kananan hukumomi 20 na jihar Kebbi.
KARANTA HAKANAN Sake Zaben Gwamnan Adamawa PDP Ta Zargi INEC
Yayin da za a sake gudanar da zaben Sanatan Kebbi ta Arewa, mazabar tarayya biyu da mazabun Jihohi takwas a jihar.
Kwamishinan wayar da kan jama’a da wayar da kan masu kada kuri’a na INEC, Mista Festus Okoye ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a wajen rabon muhimman kayayyakin zabe, ranar Juma’a a Birnin-kebbi.
Ya ce hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zabuka cikin nasara a Kebbi.
Okoye ya ce hukumar ta raba muhimman kayyakin zabe da suka hada da katunan zabe da takardar sakamako da na’urar tantance masu kada kuri’a ta (BVAS).
Ya ce Hukumar ta gudanar da aiki tare da masu ruwa da tsaki tare da wakilan jam’iyyun siyasa, kungiyoyin farar hula, kungiyoyi da hukumomin tsaro domin saukaka jigilar ba tare da wata matsala ba.
“Shugaban jami’an tsaro sun yi alkawarin cewa suna da karfin gwiwa, iyawa da kuma kayan aiki don tura isassu kuma yadda ya kamata a duk wuraren da za a sake gudanar da zaben.
“A namu bangaren, Shugaban Hukumar ya tura kwamishinonin kasa uku jihar Kebbi saboda yawan zabukan da muke da su a nan.
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Ya kuma tura ma’aikatan da za su jagoranci wannan zabe na musamman. (NAN)
A Wani Labarin Kuma ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bukaci FG Ta Bada Fifiko Kan tsaro, Ilimi Ga Mata
Yayin da kasar ke cika shekara tara da sace ‘yan mata 275 a garin Chibok na jihar Borno, gidauniyar Murtala Muhammed ta bukaci gwamnatin tarayya da ta baiwa ilimin ‘yan mata da mata fifiko a kasar nan.
Babbar Jami’ar Gidauniyar, Dakta Aisha Muhammed-Oyebode, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a a wani bangare na bukukuwan zagayowar ranar da ‘yan Boko Haram suka yi garkuwa da su a ranar Juma’a.