Kasar Misra da Lebanon a ranar Laraba sun bude tashar jiragen saman su domin ganin jiragen sun fara ayyukansu, bayan kwashe wata uku tasoshin na kulle saboda annobar cutar Korona.
EgyptAir, jirgin kasa na Misra a wani sanarwa da ya fitar ya ce zai yi aikin jigilar a kasashe 14 inda zai yi jigilar fasinjoji 2, 000.
Ya ce zai dauki fasinjoji na farko daga filin jirgin sama na ‘Cairo International Airport’ zuwa kasar Tunisia da misalin karfe 8:30 na safe (0630 GMT), kamar yadda suka tabbatar.
Kamfanin jirgin saman ya ce zai fara aiki daga wurare 29, kafin daga bisani ya fadada ayyukansa.
Tun cikin watan Maris aka rufe tasoshin jiragen saman a wani mataki na dakile yaduwar cutar Korona.
A kasar Lebanon, tashar jirgin Beirut Rafik Hariri airport, shi ne tashar jirgin sama na farko a Lebanon da aka bude, wanda zai yi aikin da bai wuce kashi goma ba. Tashar jirigin saman zai rika daukar fasinjoji 2, 000 zuwa 3, 000 a kowacce rana.
Gwamnatin Lebanon ta ce fasinjojin da za su iso kasar da ba a yi musu gwajin korona da zarar sun iso za a yi musu.