Kungiyar ‘Yan Jaridu a Nijeriya ta koka kan halin da ‘ya’yanta ke ciki yayin gudanar da ayyukansu a daidai lokacin da ake fama da annobar korona a duniya.
Kungiyar ‘Yan Jaridun tac e suna fuskantar makamancin hadarin da likitoci da sauran ma’aikatan jinya ke ciki na kamuwa da cutar ta Korona, inda tace tuni wasu ‘Yan Jaridu uku suka rasa rayukansu sakamakon harbuwa da annobar, yayin da wasu da dama suka kamu.
Shu’aibu Usman Leeman, Sakataren kungiyar ‘yan Jarida shi ne ya tabbatar da hakan a hirarsa da gidan Rediyon Faransa, inda ya ce kuma abin takaicin a daidai wannan lokaci da ‘yan jarida ke fuskantar wannan matsalar, a kuma wannan lokaci ne wasu kafafen watsa labaran ke zaftare albashin ma’aikatansu, wasu kuma na korar wasu ma’aikatansu.