Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya WFP, ta ce akalla mutane sama da miliyan 40 dake zaune a Yammacin Afirka za su fuskanci karancin abinci a watanni masu zuwa, sakamakon illar annobar korona wadda ta tilasta killace mutane a cikin gidajensu.
Kakakin Hukumar, Elizabeth Byers ta ce annobar Korona ta kuma dada fito da halin da halin kuncin da mutanen da suka bar matsuguninsu sakamakon tashin hankali da kuma wadanda sauyin yanayi ya yiwa illa.
Rahoton hukumar ya ce adadin yara ‘yan kasa da shekaru 5 miliyan 12 za su gamu da tamowa tsakanin watan Yuni zuwa Agusta sabanin sama da miliyan 8 da aka gani a irin wannan lokaci a shekarar bara.
Wannan ya biyo bayan matakan da gwamnatoci suka dauka na tilastawa mutane zama a gida domin dakile yaduwar annobar korona wacce ta shafi manoma da masu harkar samar da abinci.
Hukumar ta jaddada cewa a tsakanin watan Yuni zuwa Agusta sama da mutane miliyan 21 za su sha wahala wajen ciyar da kan su a Yankin Afirka ta Yamma, musamman a kasashen Gambia da Jamhuriyar Benin.