Hukumar lafiya ta duniya ta ce cutar Korona na iya shafar mutane kimanin miliyan 250 a Afirka tare kuma da kassara harkokin lafiya a nahiyar yayin da kawo yanzu cutar ta hallaka mutane 300,000 a duniya baki daya.
A cikin rahoton da ta fitar hukumar lafiyar ta ce matukar ba a dauki matakan gaggawa ba nan da shekara mai zuwa, cutar na iya yaduwa sosai da kuma yin mummunan illa a kasashe 47 na Afirka
Masu bincike sun ce kimanin kashi 22 cikin dari na al’ummar Afirka biliyan daya na iya kamuwa da cutar cikin shekara daya tare da wasu mutanen miliyan 37 da za su kasance dauke da cutar ba tare da ta nuna alama a jikinsu ba.