A ranar Talata ne kotun daukaka kara da ke Abuja ta ajiye hukunci kan karar da dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Sakkwato, Sa’idu Umar ya shigar, yana kalubalantar zaben gwamna Ahmed Aliyu na jam’iyyar APC.
Alkalan kotun daukaka kara mai mutane uku sun ajiye hukunci har zuwa ranar da za a sanar da bangarorin da lamarin ya shafa bayan amincewa da dukkan shaidu.
Karanta nanGwamnan Jigawa Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Biliyan 298 Ga Majalisar Jahar
Yayin da Sunday Ibrahim Ameh (SAN) da ke wakiltar wadanda suka shigar da kara ya roki kotun da ta samu cancantar daukaka karar kuma ta ba su damar, Cif Wole Olanipekun (SAN) da Dokta Hassan Liman (SAN) da kuma I. S. Mohammed da ke wakiltar wadanda ake kara na daya zuwa na hudu sun bukaci kotun yin watsi da daukaka karar.
Tare da tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Sokoto wadda ta bayyana Aliyu a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar.
Idan dai ba a manta ba, kwamitin mutane uku na alkalan kotun sauraren kararrakin zabe karkashin jagorancin Mai shari’a Haruna Msheila, sun yi watsi da karar da jam’iyyar PDP da dan takararta na gwamna suka shigar a ranar 30 ga watan Satumba, a zaben gwamnan da ya gabata. a jihar Sokoto.
Kotun ta ce wadanda suka shigar da karar sun kasa tabbatar da dalilai guda shida da aka tsara a cikin karar da suka shigar na hadin gwiwa.
A wani labarin kumaGwamnatiin Jahar Zamfara Ta Ayyana Dokar Ta Baci Akan Harkar Ilimi A Jahar
A cewar kotun, dalilan da aka bayyana a cikin karar sun shafi rashin cancantar Aliyu da mataimakinsa ne, da karya takardun shaida, bambamcin sunayensu, magudin zabe da kuma rashin bin ka’idojin zabe.
Karamar kotun ta yanke hukuncin cewa wadanda suka shigar da karar ba su iya tabbatar da zargin ba bisa ka’ida ba kamar yadda doka ta tanada, domin kashi 70 cikin 100 na shaidun da suka gabatar bai dace ba saboda suna da alaka da zabukan ‘yan majalisar jiha da aka gudanar a rana guda.