Kungiyar Kiristocin Najeriya CAN, ta ce ba ta da masaniyar Naira biliyan biyu da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour LP, Peter Obi ya ba coci-coci.
An tattaro cewa wani koke da ya yi ta yawo a shafukan sada zumunta ya yi ikirarin cewa Obi ya bai wa coci-coci Naira biliyan biyu ta hannun kungiyar CAN don taimakawa jama’arsu su zabe shi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Da Dumi-Dumi: Southampton ta kori kocinta Nathan Jones
Shugaban CAN, Daniel Okoh, a wata sanarwa a ranar Lahadi, ya musanta ikirarin.
Ya ce kungiyar ba ta jam’iyya ba ce, kuma ba za ta amince ko hada kai ga kowane dan takara ba.
“An jawo hankalin shugabannin kungiyar kiristoci ta kasa (CAN) a kan wata wasika da ake yadawa a yanzu haka a shafukan sada zumunta, inda ake zargin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi ya ba da wasu kudade har Naira biliyan N2bn ga Majami’u a karkashin inuwar CAN,” in ji sanarwar.
“Ina amfani da wannan kafar wajen bayyana cewa, takardar da ake kira takardar koke da wani Fasto Frank Onwumere ya sanya wa hannu kuma aka aika wa ofishina ba ta da ma’ana kuma za a iya kwatanta shi a matsayin yunkurin da bai yi nasara ba na jawo kungiyar Kiristoci ta shiga harkar siyasa a 2023. .
“Duk da haka, za mu binciki madogarar wasikar domin amfanin jama’a.
“Don daidaita bayanan, ban san wani batun Naira biliyan N2bn da aka bai wa Coci-coci a Najeriya don tara kuri’u ga kowane dan takarar shugaban kasa a 2023 ba kuma ban taba samun wannan takarda ta ranar 22 ga watan Disambar shekarar 2022 ba.
“Ya kamata ‘yan Najeriya su lura cewa kungiyar CAN a matsayinta na mai imani, ta tsaya tsayin daka a matsayinta na ba ta jam’iyya ba, kuma ba za ta amince ko kuma hada goyon bayan duk wani dan takara a zabe mai zuwa ba kamar yadda wasu ‘yan siyasa ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani don bata sunan ta da hoto
“Saboda haka, CAN ta bukaci jama’a da su yi watsi da wasiƙar da aka ce ta shigar domin abin da ke cikinta ba gaskiya ba ne, amma na mugunta ne.
“Muna gargadin masu yin karya da su daina irin wannan aika-aikar domin suna iya bata sunan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da kuma cibiyoyin addini da ake girmama su da kuma lalata zaman lafiyar jama’a.”
Kazalika, kungiyar kamfen din Obi-Datti ta kuma yi watsi da karar da ake zargin, tana mai bayyana ta a matsayin “kayan bakar fata”.
Har ila yau, Frank Onwumere ya musanta rubuta takardar koke kan zargin karkatar da Naira biliyan 2 da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya ba majami’u a karkashin inuwar kungiyar Kiristoci ta Najeriya.
Onwumere ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, inda ya ce bai taba rubuta irin wannan koke ba kuma bai ba kowa damar yin hakan a madadin sa ba.
A wani labarin kuma, Da Dumi-Duminsa: DSS Ta Gayyaci Fani-Kayode Kan Rahoton Juyin Mulki
Hukumar tsaro ta DSS, ta gayyaci mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC PCC, Femi Fani-Kayode bisa zargin yunkurin juyin mulki gabanin zaben watan Fabrairu.
Fani-Kayode ya tabbatar da gayyatar da hukumar DSS ta yi masa a wata sanarwa a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa zai amsa gayyatar da safiyar yau Litinin.