Gwamnatin jihar Adamawa ta ce adadin wadanda suka kamu sakamakon barkewar cutar kwalara ya haura sama da mutane 500, yayin da aka samu adadin wadanda suka mutu sanadiyar cutar zuwa 23.
Ta kara da cewa tun bayan barkewar cutar a watan Satumba, iyali daya da aka yi wa maganin kwalara sun rasa yara uku.
Daraktan Ma’aikatar Kiwon Lafiyar jihar, Dakta Celine Laori ce ta tabbatar da hakan a jiya Talata a Yola babban Birnin jihar.
Laori ta ce kananan hukumomin da abin ya fi shafa sun hada da Yola ta Arewa, Girei, da kuma Lamurde.
KARANTA WANNAN LABARIN: Babbar Jikan Sir Ahmadu Bello Sardauna ta Rasu
“Tun bayan barkewar cutar a jihar a watan Satumba har zuwa yau, mun samu rahoton mutane 500 da ake zargi da kamuwa da cutar, da kuma mutuwar mutane 23.
Ta yi kira ga mutanen jihar da su kula da tsaftar muhalli da tsaftar muhalli tare da tabbatar da cewa, abinci da ruwan da za a sha sun kasance cikin tsafta.
Awani Labarin Kuma na daban.
Jami’an ‘yan sanda da ke aiki a rundunar‘ yan sandan jihar Ondo sun kama wani Fasto mai shekaru 61, Mai suna Famakinwa Ajayi.
An kama shi ne bisa zargin yiwa wata yarinya ‘yar shekara 16 fyade, da kuma yi mata ciki.
Malamin Majami’ar, a cewar ‘yan sanda, ya aikata wannan aika -aikar ne da nufin cewa yana yi mata Addu’a.
Lamarin ya faru ne a garin Ogbese da ke karamar hukumar Akure ta Arewa a jihar.
Da take gabatar da wanda ake zargin a gaban manema labarai a Akure, babban birnin jihar, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Misis Funmi Odunlami, ta ce, za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu, bayan an kammala gudanar da bincike.
Odunlami ta kuma Kara da cewa, wanda abin ya rutsa da ita, ta ba da labarin yadda wanda ake tuhuma ya taba lalata da ita a cikin gidansa, sannan daga baya ya dauke ta zuwa kasuwa da daddare, kuma ya yi amfani da ita.
Ta ce, “Famakinwa Ajayi mai shekaru 61 wanda limamin Coci ne, ya yiwa ‘yar shekara goma sha shida ciki.”
A cewarta, wanda ake zargin ya furta cewa ya kwanta da Budurwar sau daya, a cikin dakinsa.
“Za a gurfanar da shi a gaban kotu don fuskantar Hukuncin da ya dace dashi,” in ji ta