Bayan kwana uku da wani hatsarin kwale-kwale ya afku a kusa da unguwar Ikorodu a jihar Legas, inda fasinjoji biyu suka mutu, wani hatsarin kwale-kwale ya sake afkuwa a daren Juma’a a unguwar Mile 2.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da Misis Sarat Braimah, Manajan yankin Legas, na hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa (NIWA) ta fitar ranar Asabar.
Ta sanar da cewa, har yanzu ba a gano fasinjoji 16 da ke cikin kwale-kwalen ba.
“Da misalin karfe 7.45 na rana, ranar 8 ga watan Yuli, hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa da hukumar kula da hanyoyin ruwa ta jihar Legas, sun samu kiran gaggawa kanamarin da da ya faru a magudanar ruwa.
“Wani jirgin ruwan fiber na fasinja na W19 dauke da mutane kusan 16 ke ciki, ya kife a yankin Ojo da ke jihar.
“Jirgin ruwa daga Mile 2 zuwa Ibeshe a cikin axis Ojo ya karya ka’idojin magudanan ruwa na tafiya da wuri ta hanyar tashi da karfe 7.45 na yamma,” in ji ta.
Braimah ya ce, igiyar ruwan ne ya sa kwale-kwalen ya kife.
“An ce duk fasinjojin da ke cikin jirgin, ciki har da yara, ba duka suke sanye da rigar ceto na ruwa ba.