By Ishaq Dabai
Rikici ya barke da sanyin safiyar ranar Lahadi, lokacin da ake fargabar masu ibada guda shida sun mutu bayan wata babbar wayar wutar lantarki ta tarwatse ta fada kan wadanda abin ya rutsa da su yayin da ake tsaka da gudanar da Ibada a cocin ranar Lahadi.
A halin da ake ciki ba za a iya tantance ainihin wadanda suka mutu ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.
A cewar wani ganau, lamarin ya faru da misalin karfe 07:34 na safe a kan El-Adonai Evegenlical Ministry ta18 dake kan titin Jibiwu zuwa titin off Agbe, da kuma madakatar motoci ta U-turn , Abule Egba, Lagos.
Lamarin ya kunshi, wani babban tashin hankali da ya hada Cherum da Saraphim, da kuma C&S, sandar tutar Cocin da ke haifar da girgiza wutar lantarki inda ta hada dawasu maza 6.
A halin yanzu, mazauna tashar wuta ta Agege da hukumar kashe gobara ta jihar Legas a halin yanzu suna gudanar da binciken lamarin da nufin kare rayuka da dukiyoyi a yankin.
Daraktan Hukumar Kashe Gobara da bada Agaji ta Jihar Legas, Misis Adeseye Margaret,ya tabbatar da afkuwar lamarin duk da haka ba’a iya gano adadin wadanda suka mutu ba ya kara da cewa wasu daga cikin wadanda abin ya rutsa da su ba su san komai ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.
Adeseye yace “An sanar da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ikeja don haka yaba da damar Dauke wutar lantarki ga muhalli yayin da ayyukan ceto ke ci gaba da kasancewa a cikin natsuwa da tashin hankali na matasa,” in ji Adeseye.