By Abbas Yakubu Yaura
Wani ma’aikaci a majalisar dokokin kasar ya zame ya fadi a kan wata matattakala ya mutu a ranar Litinin.
Shaidun gani da ido sun ce Abdul Abayomi, mai shekaru 34, ya takure ya fadi a kan benen a lokacin da yake hawa na biyu na bangaren fadar majalisar dokokin kasar.
Masu tsaftar muhalli da suka gan shi lokacin da ya fadi, an ce sun sanar da wasu ma’aikatan da suka zo taimakonsa nan take.
An ce abokan aikinsa sun kai shi asibitin majalisar dokokin kasar domin kula da lafiyarsa amma ya rasu a hanya.
An ce ya mutu ne sakamakon bugun zuciya da wasu cututtukan da ke karkashin kasa.
Marigayin yana aiki ne a Sashen Inter-Parliamentary a karkashin hukumar kula da harkokin majalissar dokoki ta kasa.
An ce ya yi aure ne a ranar 4 ga watan Disamba, 2021. Yayin da yake daga jihar Osun, an ce matarsa ‘yar jihar Delta ce.
Har ila yau, an ce wani ma’aikacin wucin gadi ya fado daga kangi a lokacin da yake aiki a hawa na hudu na harabar majalisar dokokin kasar wanda hakan ya sa ya yanke masa wuya sosai, baya ga wasu raunuka.
An ce an kai ma’aikacin asibitin kasa inda yake jinya.sannan ma’aikacin da ya jikkata yana cigaba da samun sauki.
Da aka tuntubi Daraktan Yada Labarai na Majalisar Dokta Emmanuel Agada, ya ce ba zai iya tabbatar da mutuwar ba tunda bai samu wani bayani a kai ba.
“Gaskiya, na bar ofishin ne kawai amma ban samu irin wannan bayani kan lamarin ba. Don haka ba ni da ikon tabbatar da labarin a yanzu,” in ji Agada.