Ma’aikatan karamar hukumar Lantang ta Arewa da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun rufe sakatariyar karamar hukumar.
Wasu daga cikin fusatattun ma’aikatan da suka zanta da jaridar PUNCH a Jos, sun ce sun yanke shawarar rufe sakatariyar ne domin yin rajistar kokensu kan rashin biyansu albashi sama da watanni hudu.
KARANTA WANNAN LABARIN: CAN ta yi magana mai zafi kan sanya Sunan Manyan Limaman ta a Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓe na Tinubu-Shettima
Ɗaya daga cikin ma’aikatan da ta ki bayyana sunanta ta ce, “da sanyin safiyar yau (Alhamis), ma’aikatan karamar hukumar Langtang ta Arewa da dama sun gudanar da zanga-zangar lumana domin yin rajistar kokensu na rashin biyansu albashin watanni shida da karamar hukumar ta yi.
“An rufe sakatariyar karamar hukumar ne a karkashin umarnin kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi ta kasa. An rufe dukkan ofisoshi, na kananan hukumomi da na tarayya, har da ofisoshin shari’a.
Ta kara da cewa “Hanyoyin shiga da fita daga Langtang ta Arewa kuma an rufe su na tsawon sa’o’i da dama kuma ba mu shirye mu dakatar da zanga-zangar ba sai dai idan gwamnati ta biya bukatunmu.”
Shugaban kungiyar ta NULGE a jihar Makwi Yohanna shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce, “Ba na zargin ma’aikata saboda mai yunwa mutum ne mai fushi.
A wani labarin kuma:An nemi Ƴan Takarar Shugaban Ƙasa Su dakatar da Kamfen nasu kan wani Dalili
An bukaci daukacin ‘yan takarar zaben shekarar 2023 da jam’iyyunsu da su dakatar da yakin neman zabensu, su koma yankunansu domin taimakawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.
Darakta Janar, Sabon Dream for Grassroots Development, Onwubuya Abrahim Breakforth, ya yi wannan kiran a Abuja ranar Alhamis bayan taron gaggawa na kungiyar da kuma jawabin na kasa.