Yayin da Tshohon mataimakin shugaban kasa Kuma Dan takarar shugaban cin kasar nan a 2019, ya zargi Lai Muhammad, kan cewa wai yana da hannu kan yinkurin juyin mulki inda ya bayyana Atiku a matsayin Wanda yake cin dunduniyar Gwamnati da yi musu bita da Kulli.
Sai dai Atiku yace baiyi mamakin wannan zance daga bakin na Lai, ba Dan ya kware kan karya Dan hakan PDP tace sai ya fada mata dalilin da yasa yake wa Atiku bita da kulli da yada jita-jita.
Mai magana da yawun Atiku mista Paul Ibe, yace lai Muhammad yayi kaurin suna gun karya duk da watan Ramadana ne inda har sai da mataimakin shugaban kasa yace mai Yasa lai baya canja hali duk da ana Ramadan.
Mutanen da suka dauki lai Muhammad aiki amma suna gani har a wata mai alfarma karya yake kuma yake zargin cikakken Dan Dimokuradiyya -inji shi
Inda yace ai Shugaba Muhammad Buhari ya taba kifar da zababbiyar Gwamnati amma yanzu wa yake cewa komai akan abun.
A karshe Ibe, yace Atiku ya bada gudunmuwa sosai Dan dorewar Dimokuradiyya a kasar, nan, ya cigaba da cewa Kamata ya yi Lai Muhammad, ya koma ya ji da badakalar kudade a ma’aikatar yada labarai, ba Rika yin Soki Burutsu ba.