Kungiyoyin jami’o’in da ke yajin aiki da suka hada da kungiyar malaman jami’o’i da manyan ma’aikatan jami’o’in Najeriya, sun koka da yadda tsarin rashin aikin yi ba tare da biyan albashi ba da gwamnatin tarayya ta bijiro da shi.
A cewar su, suna zargin an yi hakan ne domin ganin an tilasta musu, wajen janyewa daga kudurinsu.
Shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke; da Mataimakin Shugaban SSANU na kasa, Dr Abdussobur Salaam, ne suka bayyana hakan yayin ganawar su da manema labarai.
Osodeke ya shaida wa cewa a karon karshe da ya karbi albashin shi ne a cikin watan Fabrairu, inda ya kara da cewa dabarun gwamnati na hana su albashin na nufin rage musu azama kan bukatun kungiyar.
Sai dai ya ce ‘ya’yan kungiyar za su ci gaba da dagewa ko da kuwa za su yi aikin da bai dace ba ko kuma su shiga noma don samun kudi.
Ya kara da cewa makonni uku bayan sun yi ganawar karshe da kwamitin sasantawa, ba a ji komi daga gwamnati ba.
Ya ce, “Ba mu ji komai daga gwamnati ba. Wannan dai shi ne mako na uku da kammala taron da kwamitin sasantawa karkashin jagorancin Farfesa Briggs.
Za mu ci gaba da jira har sai sun amsa. “Ngige ya yi imanin cewa mambobinmu za su ji yunwa su roke su, amma ba za mu roke su ba, a shirye muke mu jira shekara guda, shekaru biyu, har sai sun amsa.
Wani lauya, Mista Oluwafemi Olabisi, ya ce rashin adalcin aiki ne rashin biyan ma’aikata albashi yayin da suke yajin aiki.
Ya ce, “Halin da ake hana ma’aikata samun albashi shi ne lokacin da babu wata alaka tsakanin ma’aikata da ma’aikata.
“Amma idan ma’aikata sun gaza yin aiki ko yajin aikin kwas ko tada zaune tsaye, kamar yadda ASUU da sauran ma’aikatan jami’o’in ke yi, ba za a iya dakatar da su ba yayin da suke yajin aiki kuma ba za a iya dakatar da albashinsu ba.