By Abbas Yakubu Yaura
Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kai hari a ranar Asabar a karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.
Rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun ce adadin wadanda aka yi garkuwa sun kai sama da mutane hamsin yayin da aka hallaka wata mace guda daya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Neja: Wasu ‘Yan Daba Sunyi Dirar Mikiya A Wurin Liyafar Aure Tare Da Awon Gaba Da Wayoyin Hannu
Sai dai har yanzu rundunar ‘yan sandan ba ta tabbatar da faruwar lamarin ba, sama da sa’o’i 24 bayan kisan gillar da aka yi, kamar yadda wasu kiraye-kirayen da aka yi wa rundunar ‘yan sandan jihar Sakkwato, PPRO, Abubakar Sanusi, bai amsa ba, haka kuma bai amsa sakon tes da aka aika masa ba.
Wata majiya da ta so a sakaya sunanta ta shaida wa wakilinmu cewa an kashe matar wani Dagacin kauye tare da yin garkuwa da mutane da dama a wani daurin aure da aka yi a karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto a yammacin ranar Asabar.
A cewar majiyar, “’yan bindigar sun ja hankalin mahalarta babban taron baki daga garuruwa masu nisa da na kusa da su zuwa Gebe. Matar shugaban kauyen ita kadai aka kashe saboda ta ki yarda a sace ta.
“ Ita kadai ce aka kashe kamar yadda na sani lokacin da ta tsaya tsayin daka cewa ba za ta bi ‘yan bindigar zuwa maboyarsu ba.
“Baya ga wadanda aka yi garkuwa da su aka tafi da su zuwa wuraren da ba a san ko inane ba, wasu da dama sun samu raunuka a kokarinsu na tserewa daga sace su.”
Comments 1