A halin yanzu mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ne ke jagorantar taron majalisar tattalin arzikin kasa na farko a shekarar 2022 a dakin taro na gidan gwamnati (Old Banquet Hall), Abuja.
Mambobin majalisar sun hada da gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele; Sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Boss Mustapha; Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Mohammed Bello da gwamnonin jihohi 36.
Taron na NEC yana samun halartar wasu gwamnonin jihohi yayin da wasu ke halartar ta allon gani daka daga jihohinsu.
Wadanda suka halarci taron sun hada da Gwamna Hope Uzodinma (Imo), Yahaya Bello (Kogi), Kayode Fayemi (Ekiti), Willie Obiano (Anambra), Doye Diri (Bayelsa), Babagana Zulum (Borno), Babajide Sanwo-Olu (Lagos) da Emmanuel Udom (Akwa-Ibom).
Ana sa ran fitar da sanarwar a karshen taron bayan da hukumomin gwamnati da abun ya shafa suka yi musu bayani kan shirye-shiryen tattalin arziki na gwamnati.
Hukumar zabe mai zaman kanta a duk wata tana da ikon ba shugaban kasa shawara kan harkokin tattalin arzikin kasa.