An kashe fararen hula biyar lokacin da ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai farmaki a wani kauye da ke Arewa mai nisa a kasar Kamaru, in ji majiyoyi daga Hukumomin tsaron kasar.
Wasu gungun ‘yan ta’adda na Boko Haram dauke da muggan makamai a kan babura sun kai hari a kauyen Assigachia, da ke yankin Mayo Moskota a arewa mai nisa, kilomita kadan daga kan iyakar Nigeria, a cewar kwamandan yankin Janar Bouba Dobekreo.
Tun daga shekarar 2014, yankin kasar Kamaru ta tsakiyar Afirka, ta shiga yaki da ‘yan ta’addan Boko Haram a cikin yankin na Arewa mai nisa.
Tawayen Boko Haram ya fara ne a tun a shekarar 2009 a Arewa maso gabashin Nigeria, kafin ya bazu zuwa kasashen makwabta. Tun daga wannan lokacin, sama da mutane 36,000 (galibi Yan Nigeria) aka kashe, kuma sama mutane miliyan 3 sun tsere daga gidajensu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Shugaba Buhari ya shiga Zauren Majalissar don Gabatar da Kasafin 2022
Sai da a bangaren hukumomin kasar Kamaru kuwa, samar da kuɗi wurin yakar matsalar tsaro ya kasance babban ƙalubalen, wurin yaƙi da ‘yan ta’adda.