Mutane 10 suka mutu sakamakon mummunan hatsari da ya auku a titin Kaura Namoda zuwa Gusau dake jihar Zamfara. Kamar yadda Kakakin ‘yan sandan jihar, SP Muhammad Shehu ya shaidawa Daily Trust.
Ya tabbatar da cewa; motar Tirela dauke da fasinjoji da kayayyaki a cikinta wacce ta fito daga kasuwar Daji ta samu mummunan hatsari inda mutum 10 suka rasa ransu a wurin, yayin da mutane 45 suka raunuka daban-daban inda aka kai su asibitin FMC dake Gusau.
Ya ce wadanda suka rasa ransu, tuni aka kai su wurin ajiye gawarwaki na asibitin Gusau, inda kuma daga bisani za a mikawa iyalansu domin jana’izarsu.
Kwashinan ‘yan sandan jihar, Usman Nagogo ya bada umurnin a yi binciken hatsarin. Inda kuma ya taya iyalan wadanda suka rasa ransu ta’aziyyah.