Rahotanni sun tabbatar da cewa; musulmi kimanin dubu goma ne wadanda suka kasance ko ‘yan asalin kasar ko kuma baki da ke zaune a cikin kasar ne za su samu damar gudanar da aikin hajjin bisa wasu tsauraran ka’idoji da aka gindaya a yayin gudanar da ibadar.
A Saudiyya, maniyyata sun shirya soma gudanar da aikin hajjin bana duk da annobar cutar korona wanda ta janyo takaita yawan al’ummar Musulmin da ke da niyyar zuwa.
Saudiyya ta kasance daya daga cikin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya da ake da yawan Alkaluman masu cutar ta korona, inda tuni cutar ta kashe mutum dubu biyu da dari bakwai da talatin da uku daga cikin sama da dubu dari biyu da sittin da ta kama.
Wannan shi ne karon farko da ake daukar mataki na hana maniyyata daga sauran kasashen duniya shiga aikin hajjin a tarihi. Ma’aikatar shirya aikin hajjin dai, ta ce ya zama dole a yi hakan, saboda fargabar yada cutar Coronavirus.