Gwamnan jihar Filato, Simon Lalong, ya bayyana yadda ya zama darakta-janar na kungiyar yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu.
Lalong ya ce sabanin yadda ake zage-zage da ake yi a wasu bangarori, nadin nasa ba diyya ba ne ga al’ummar Kiristocin Arewa saboda rashin nasarar da suka samu a zaben dan takarar mataimakin shugaban kasa.
Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja a wani bangare na kokarin nuna nasarorin da ya samu a ofis da kuma yin tir da ra’ayin da jama’a ke yi na cewa an zabe shi ne ya jagoranci yakin neman zaben jam’iyyar APC saboda matsalar da ta shafi tikitin jam’iyyar Musulmi da Musulmi, Lalong ya ce Gwamnonin Arewacin kasar nanNGF ne suka zabe shi saboda dabarun da ya yi amfani da su wajan daga matsayin kungiyar.
Da yake bayyana hakikanin abin da ya faru, gwamnan ya ce bayan dan takarar jam’iyyar ya tsayar da abokin takararsa, gwamnonin APC sun gana da shi domin tattauna yadda za a yi nasara a gaba.
Kada wani ya kuskura wajen cewa gwamnatin tarayya bata kokari kan yan Ta’adda – Garba Shehu
Ya ce gwamnonin sun shaida wa Tinubu cewa sun yi fafutukar ne don neman shugabancin kasar ya koma Kudu kuma ana sa ran za a tuntubi wasu yan siyasa domin neman dan takarar mataimakin shugaban kasa da kuma babban daraktan kwamitin yakin neman zaben.
“Dukkan su sun amince cewa in jagoranci yakin neman zabe saboda ni ne shugaban kungiyar NGF, haka kuma saboda ni ne na kai su wurin shugaban kasa domin ya ce dole ne dan takarar shugaban kasa ya koma Kudu. Don haka ana kallona zabina a matsayin wani abu. Ba ya cikin la’akari da addini,” inji shi.